Ƙarin bayani: https://hausadictionary.com/HausaRadio.net/2026-05-27
== BBCHausa Safe 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Aisha Sharif Baffa
#1 🎧 @0:17 Lebanon ta ce an kashe mutane talatin da ɗaya a hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a jiya Talata.
#2 🎧 @0:26 Ghana ta fara mayar da ɗaruruwan ƴan ƙasarta gida daga Afirka ta Kudu bayan zanga-zangar ƙyamar baƙin haure.
#3 🎧 @0:31 A Najeriya, yayin da ake ci gaba da dakon sakamakon zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC, jam’iyyar ta yi ƙarin haske kan abin da ya janyo jinkiri wajen sanar da sakamakon.
#4 🎧 @1:03 BBC Hausa ta ce za a ji ƙarin bayani kan abubuwan da ya kamata mai zuwa Sallar Idi ya yi, da kuma wanda zai yi layya.
== BBCHausa Hantsi 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Aisha Sharif Baffa
#5 🎧 @1:27 Ma’aikatan kamfanin lantarki na Samsung sun dakatar da yajin aikin da suka shiga bayan cimma matsaya kan biyan su kuɗaɗen alawus.
#6 🎧 @1:41 A Najeriya, bayan tsohon ministan sadarwa Farfesa Ali Isa Pantami ya rasa damar zama ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Gombe, ya sauya sheƙa zuwa PDP inda aka ba shi takarar.
#7 🎧 @2:11 A Najeriya, manoma da dama na barazanar ƙin noma kayan abinci kamar masara da gero, suna cewa za su fi mayar da hankali kan noman kayan sayarwa kamar waken soya da gyada.
== BBCHausa Rana 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Aisha Aliyu Jafar
#8 🎧 @3:22 Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo na cikin hali na tsaka mai wuya, inda take fama da ɓarkewar cutar Ebola da kuma rikici.
#9 🎧 @3:37 Ghana ta kwashe rukunin farko na ƴan ƙasarta daga Afirka ta Kudu sakamakon zanga-zangar ƙyamar baƙin haure.
#10 🎧 @3:47 A Najeriya, Majalisar Ba da Shawara kan Harkokin Jam’iyyun Siyasa ta buƙaci Shugaba Tinubu ya ƙara himma wajen yaƙi da ta’addanci da ayyukan ‘yan bindiga a faɗin ƙasar.
#11 🎧 @4:12 Al’ummar Musulmi na ci gaba da gudanar da shagulgulan bikin Babbar Sallah a faɗin duniya, duk da ƙorafe-ƙorafe kan tsadar rayuwa da ta hana wasu yin layya.
== BBCHausa Yamma 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Aisha Aliyu Jafar
#12 🎧 @5:23 Rundunar sojin Isra’ila ta bai wa al’ummar da ke zaune a baki ɗayan kudancin Lebanon umarnin ficewa.
#13 🎧 @5:34 Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi kira da a tsagaita wuta a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo domin samun damar dakile yaɗuwar Ebola.
#14 🎧 @5:43 A Najeriya, masana tsaro sun fara tsokaci kan rahoton Amurka da ke cewa a ƴan shekarun nan wasu masu gwagwarmaya da makamai daga tsatson Fulani na kai miyagun hare-hare kan al’ummomi.
#15 🎧 @6:14 A Najeriya, ranar 27 ga watan Mayu ta kasance Ranar Yara, inda ake tambayar halin da yaran ƙasar ke ciki a ɓangarorin ilimi, lafiya, zamantakewa da tsaro.
== DWHausa Safe 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Muhammad Awal Balarabe
#16 🎧 @7:19 Musulmai a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya na hawan Sallah cikin halin ɗar-ɗar sakamakon barazanar hari da hukumomi suka ja hankali a kai.
#17 🎧 @7:37 DW Hausa ta ce za a ji abubuwan da Musulmi ya kamata ya yi a ranar Idi.
#18 🎧 @7:41 Gwamnatin Ghana ta buɗe ƙofofinta ga ɗaukacin ƴan nahiyar Afirka ta hanyar ba da visa kyauta.
#19 🎧 @7:49 A Sudan, tsadar man fetur na barazanar jefa ƙasar cikin matsananciyar ƙarancin abinci.
#20 🎧 @7:54 Za a ji inda aka kwana game da shirin Shugaba Trump na gindaya wa baƙi tsauraran sharuɗɗa kafin ba su katin zama ɗan ƙasa.
#21 🎧 @8:13 Al’ummar Gaza na gudanar da Idin Babbar Sallah cikin mawuyacin hali sakamakon lalacewar gine-gine da tsadar rayuwa.
#22 🎧 @8:20 Iran ta zargi Amurka da karya matakin tsagaita wuta da ke tsakaninsu bayan hare-haren da aka kai mata ta sama.
#23 🎧 @8:24 Koriya ta Arewa ta yi gwajin sabbin makamai masu linzami masu amfani da fasahohi iri daban-daban.
== DWHausa Rana 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Musa Tijjani Ahmad
#24 🎧 @8:54 Al’ummar Musulmi a faɗin duniya na gudanar da bikin Sallar Idi a yanayi daban-daban.
#25 🎧 @9:04 Shugaban mulkin sojan Jamhuriyar Nijar, Janar Abdurrahman Tchiani, ya yi Sallar Idi a birnin Yamai.
#26 🎧 @9:08 Al’ummar jihar Borno a Arewa maso Gabashin Najeriya sun gudanar da Sallar Idi cikin yanayin cikakken tsaro sakamakon barazanar kai hare-haren ta’addanci.
#27 🎧 @9:17 Amurka ta sake jaddada zargin cewa wasu makiyayan Fulani sama da dubu talatin na da hannu a tashe-tashen hankulan da ke faruwa a Najeriya, yayin da shugabannin makiyaya ke mayar da martani.
#28 🎧 @10:18 Isra’ila ta yi iƙirarin kashe shugaban wani ɓangare na ƙungiyar Hamas a zirin Gaza.
#29 🎧 @10:23 Tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy ya buƙaci a wanke shi daga zargin hannu a badakalar zaɓen Libya.
#30 🎧 @10:30 An ceto mutanen da ambaliya ta rufe a kugu tsawon mako guda a Thailand.
== DWHausa Yamma 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Musa Tijjani Ahmad
#31 🎧 @10:58 An gudanar da Sallar Idi cikin yanayi na fargabar tashe-tashen hankula a wasu yankunan Gabas ta Tsakiya.
#32 🎧 @11:05 A jihar Kano ta Najeriya, babban abin da ya fi ɗaukar hankali shi ne bai wa sarakuna biyu cikakken ikon gudanar da Sallar Idi.
#33 🎧 @11:32 Gwamnatin jihar Legas ta bijiro da tsarin kare haƙƙin masu zama a gidaje da shagunan haya a birnin domin kare su daga barazanar masu dukiya.
#34 🎧 @11:41 Ƙasar Senegal ta shiga wani yanayi na tsaka mai wuya bayan takun-saka tsakanin Shugaba Bassirou Diomaye Faye da tsohon Firayim Minista Ousmane Sonko.
#35 🎧 @12:16 Dakarun Isra’ila sun kashe sama da mutane talatin a wani farmaki kan wasu yankunan ƙasar Lebanon.
#36 🎧 @12:22 Shugaban Amurka Donald Trump ya yi watsi da wani rahoton yarjejeniyar zaman lafiya da Iran.
#37 🎧 @12:27 Ƴan ƙasar Ghana ɗari uku sun koma gida daga Afirka ta Kudu bayan hare-haren ƙyamar baƙi.
== RFIHausa Yamma 2026-05-27 ==
Mai gabatarwa: Hawa Halliru Gwangwazo
#38 🎧 @12:36 Amurka ta gano yadda wasu ƴan ta’adda fiye da dubu talatin ke ƙaddamar da hare-hare a sassan Najeriya.
#39 🎧 @12:45 Ƙungiyar Human Rights Watch ta zargi Daular Larabawa da ɗaukar hayar sojojin Colombia domin taimaka wa RSF a yaƙin Sudan.
#40 🎧 @12:50 Mahajjata sun gudanar da ibadar jifan shaiɗan cikin yanayi na tsananin zafi, yayin da al’ummar Musulmi ke bukukuwan Babbar Sallah a faɗin duniya.
== CRI / CGTN Hausa 2026-05-27 ==
#41 🎧 @13:39 Yawan ribar da manyan masana’antun sarrafa hajoji na ƙasar Sin suka samu a watanni huɗu na farkon shekarar bana ya ƙaru da kaso sha takwas da ɗigo biyu bisa ɗari.
#42 🎧 @13:44 An ƙaddamar da bikin gabatar da fina-finan ƙasar Sin a ƙasashen waje a Johannesburg.
#43 🎧 @13:55 Tarayyar Afirka ta yi kira da a sake ƙoƙarin raya nahiyar Afirka.

Comments
Nothing yet. Say the first thing.
Sign in to join the conversation.